Friday, July 15, 2016

SAKON GORON SALLAH DAGA JAGORAN M.P.C


DAGA JAGORAN MPC
M.P.C (MOVEMENT FOR PROGRESSIVE CHANGE)
mal kabiru abubakar
     Bayan nasarar da duniya take ganin kasar Nigeria tayi wajen hambare gwamnatin kasar wadda ta sha soke-soke daga yan adawa dangane da zargin nuna bangaranci a wajen raba albarkatun da allah ya azurta kasar dashi atsakanin johohin kasar, dakuma yin ayyukan ci gaba ta hanyar zabe abin kamantawa a idanun kasashe masu tasowa. Yayin da talakawan kasar ke cike da zumudin samun tagomashin romon demokradiya dangane dayakini akan ingancin abinda suka zaba saboda ingantaccen tarihin da ake ganin ‘yan takarkarun sun kafa abaya. Da kuma kyakykyawan zaton cewa sunsan halin da kasar take ciki kumasunsanhalin datalakawa suke ciki kuma, kuma sun san abinda talakawa suke bukata. Har kawo yanzu da gwamnatin ta shiga shekara ta biyu a zangon mulkinta talakawa basu daina zuba idon idanun ganin alamara sun sawya ga barin halin da suke ba. Alumma basu samu kulawa ta bangaren tsadar abin bukata na yau da kullum ba. ‘ya’yan talakawa basu sami yantuwa daga tsohuwar aladar ajiye fursunonin dake jiran sharia agidajen yari ba tare da an kula da yi musu sharia ba. Mun sami labarin wani yaro mai tabin hankali da yayi yunkurin gudu daga babban gidan yarin kano . wani babban jami’i a gidan yasa aka kawo mai kulki ya dinga maka masa har sai da yamutu. Mun zuba ido  muga abinda akayi akai. Ko kuma muci gaba dasanarwa duniya. Al’adar alummar wannan kasar shine duk sanda shugaba yayi wani abu ba daidai ba sai a mara masa baya musamman idan mutum yana cin moriyar gwamnatin saboda kada ludayinsa ya sauka daga kan dawo. Wannan  ba dabi’a ce ta ci da kasa gaba ba. Dole mu koyi dawo da shugabanni hayyacin su ta hanyar fadin abinda muka sani na hakikanin gaskiya. Ta hanyar lafuzza tausasa ba harigido ba.
    Yakamata shuwagabanni su cimma tabbatacciyar matsaya wajen rattaba hannu akan hukunci mai tsanani ga duk shugaban da aka same shi da wadaka da kudin al’umma. Banga dalilin da za’a saki manyan barayi su dinga yawo acikin manyan motoci da gidaje su shiga kasashen da suka ga dama da kudin alumma, a dinga tsare ‘ya’yan talakawa akan wata sata wadda bata taka kara ta karyaba. Domin a zahiri su (manyan)sune suke wawashe lalitar   kasar su kai kasashen duniya su adana,  wanda hakan ya jawo takura da rashin walwala ciki da kewayen kasar wanda hakan ya haifar da kananan sace-sace a tsakanin matasan kasar. Wata rana a unguwarmu an taba kama wani yaro ya saci risho,garin kwaki,da tukunya kai da ji kasan yunwace. Saboda ya wayigari babu wata dama dazai alkinta kansa da ita data rage masa. Duk an wawashe anje an gina wasu kasashen dasu. Dayawa akwai kasashenda ajiye-ajiyen da shuwagabannin mu suke acikin bankunan su da kuma kamfanonin da suke zuwa su kafa acan shine abinda yan kasar suke samun tattalin arzikinsu da shi. Wannan wane irin gwaranci ne, ka kashe naka ka raya na wasu. Mun samu labarin wani shugaba daya tura wasu kudi masu yawan gaske account din wani abokinsa dake ketare sai daya sauka yaje a bashi kudin shi kuma abokin nasa yace bai san zancen ba. Kunga anyi biyu babu. Ni a ra’ayi na idan har za’ayi maganin manyan sace-sace acikin gwamnati to kai tsaye anyi maganin yawan sace-sace  acikin al’umma. Domin wancan shi ya haifar  wannan. A karshe muna tabbatar wa da gwamnati cewar mun san tana iya bakin kokarinta. Hakika muna amfani da wannan damar wajen sanar da mutane cewar hakika gwamnati tana bakin kokarinta, musamman a matakin tarayya. Mu kuma a matakai na jihohi dole ne mu cire tsoro mu haska mata abubuwan dake faruwa domin ta sani ta maganta. kuma muna amfani da wannan dama wajen haskawa yan siya sa cewar mu ba ‘yan adawa bane, bama adawa  da kowacce gwamnati a siyasance. Mudai muna sa ido ne a matakin addini da , sharia da zamani. Ban kafa wannan cibiya ta M.P.C don yin adawa da gwamnati ko yiwa wani dan siyasa aiki ba. Muna yiwa shuwagabanninmu fatan Allah yayi musu jagoranci, muna fatan Allah ya warware dukkan matsatstsalun Nigeria , muna fatan Allah ya sanya wannan kasa tamu acikin jerin manyan kasas shen duniya . Allah ya kunyata makiyanmu masu son suga mun shiga cikin rudanin siyasa. wassalamu alaikum
Mal kabiru abubakar

jagoran M.P.C

No comments:

Post a Comment